21/03/2026
SADAUKARWA DAGA ACHRAF HAKIMI.
Achraf Hakimi, kyaftin ɗin Morocco, ya fito fili ya ƙi amincewa da hukuncin da Confederation of African Football (CAF) ta yanke na ba ƙasarsa kofin gasar Africa Cup of Nations 2025, yana mai cewa Senegal ce ta cancanci zama zakara bayan nasarar da ta samu a fili.
A cikin wata sanarwa mai ƙarfi, ɗan wasan baya na Paris Saint-Germain ya bayyana cewa shi da abokan wasansa bai kamata su karɓi kofin ba, duk da hukuncin da CAF ta yanke na kwace kofin daga hannun Senegal.
Hakimi ya ce:
“Mahaifiyata ta gaya min na ƙi karɓar kofin AFCON. A hukumance na ƙi karɓar kofin, kuma ina fatan abokan wasana za su yi hakan ma. Mun samu dama mu lashe shi, amma mun gaza yin hakan.”