26/03/2022
TPL USMAN NADADA: Gaskiya Matakin Nasara
Daga Alƙalamin Jikamshi
Har yau, har gobe, daga cikin ire-iren abubuwan da na karanta a karan-kai na daga Kwamishinan Filaye da Safiyo na jihar Katsina, Alhaji Usman Nadada, shi ne kokarin kwatanta adalci a yayin da ya ke mu'amala da Jama'a.
Kamar misali, zan iya tunawa a dalilin aiki na, Alhaji Usman Nadada ya yi man wani abu, da a wajen mutum biyu ne kadai Mafi akasari za ka same shi: walau dai Mahaifan ka ko kuma mutumin da ya yi riko da adalci ya Kuma kaucewa son zuciya.
Abinda ya faru kuwa shi ne wata magana da ya taba gaya man a ofishin sa lokacin ya na rike da matsayin Janar Manaja na Hukumar Tsara Birane da Yankuna: "Hajji Garba ka ga dai bakin gwargwado Allah ya yi ma ka basira da nasibi a wannan aikin na ku na Jarida.
Bakin gwargwado mutane sun san ka kuma su na respecting abinda ka ke, to shawarar da zan ba ka a nan ita ce kar ka sake ka tsugunnar da kan ka a tsarin aikin jarida na aikin gwamnati kawai, a maimakon hakan ka yi amfani da damar da ka ke da ita wajen cin moriyar baiwar da Allah Ya yi ma ka, ta hanyar kafa wata cibiya ta wannan aikin na ku mai zaman kan ta.
Ka ga kenan idan ka tashi aiki, ka na da wajen da za ka je ba wai yawo haka nan a gari ba ko zaman majalisa.
Sannan Kuma Hakan zai ba ka damar samun Yan kudaden shiga outside albashin ka. Kar ka sake a yaudare ka da wasu yan kudi da Wani zai ba ka, kashe ma ka zuciya kawai za su Yi, idan ka na da Wani private outfit har al'umma ma sai ta fi karuwa da Kai".
Ya Yi man wannan maganar daga ni sai shi a office, sannan ya maimaita man ita a wasu lokutan a tattare da sauran Yan Jarida abokan aiki na.
Irin wannan maganganun ba kasafai a kan ji su daga bakin Yan siyasa ko manyan ma'aikatan gwamnati ba.
Abinda a ka saba gani shi ne, idan an ga ka na da wata baiwa da wani Dan siyasa zai karu da ita, to fa zai san yadda zai kalallame ka ne, ya dankwarar da kai waje guda, ya Yi ta tatsar wannan baiwar ta ka don cigaban kan shi, shi kadai.
Daga ranar da ya gama cin moriyar ganga, to fa zai jefar da kwauren ta. Sanin kowane, wannan wata halayya ce da a ke kuka da ita musamman a tsakanin Yan siyasa.
Irin wannan exceptional quality, daya tamkar da goma, da na gani da Ido na daga Usman Nadada, ita ce ta sanya har yau, har gobe ni ke ganin kimar shi da mutuncin shi, domin na san ba ni kadai ya taba yi ma ita ba, ya yi ma wasu ma a gaba na.
Don kara tabbatar man da cewa, da gaske ya ke a shawarar da ya ba ni, a lokacin da na yi joining Ziima Communication a matsayin jami'in tuntuba, har Ziima din Alhaji Usman Nadada ya je, ya yi program, ya Kuma Yi ma na fatan alheri da cigaba a business din mu.
Ko shakka babu, mu na da bukatar mutane ma su irin wannan kyakyawar zuciyar a cikin wannan al'ummar ta mu.
A nawa lissafin, ba lallai ba ne sai da babban mukami Alhaji Usman Nadada zai taimaki al'umma ko gina matasa ba, ya na yin Hakan tun kafin ya shiga siyasa tsundum.
Shi ya sa idan na tashi addua, ni kan ce, abinda ya ke shi ne mafi alheri ga Alhaji Usman Nadada da al'ummar jihar Katsina, Ubangiji Ta'ala Ya tabbatar da shi, don kuwa mu kan so abu sai ya zamo ba shi ne mafi alheri ba, sannan mu ki abu a karshe ya zamo shi ne mafi alherin.
Ya Allah Kai ne mafi sanin alkhairi, Allah ga Alhaji Usman Nadada.