26/05/2026
Manchester United da Manchester City na cikin kungiyoyin da ke sa ido kan matashin dan wasan tsakiya na Nottingham Forest, Elliott Anderson, bayan rahotanni sun bayyana cewa kungiyar na iya sauraron tayin sayar da shi a wannan kasuwar cinikayya mai zuwa. Dan wasan dan asalin Ingila ya janyo hankalin manyan kungiyoyi sak**akon bajintar da yake nunawa a kakar bana.
A cikin wasanni 17 da ya jagoranta, mai horaswa Micheal Carrick ya samu maki 39 tare da Manchester United, inda kungiyar ta yi nasara a wasanni 12, ta yi kunnen doki sau 3 sannan ta sha kashi sau biyu kacal tun daga watan Janairu.
Bayan cire Lewis Hall daga tawagar kasar Ingila, Manchester United na ci gaba da bibiyar halin da dan bayan Newcastle ke ciki, domin dade tana nuna sha’awar daukarsa zuwa Old Trafford.
Manchester United na kuma kokarin tabbatar da Bruno Fernandes ya ci gaba da zama a kungiyar duk da rade-radin da s**a bayyana a baya kan yiwuwar barinsa a karshen kakar wasa kan farashin kusan fam miliyan 55. Bruno ya taka rawar gani sosai a kakar bana, inda ya kafa tarihi a gasar Premier League tare da lashe kyautar gwarzon dan wasan kungiyar da sauran lambobin yabos.
A gefe guda kuma, Barcelona ta shiga tattaunawa da Manchester United domin ci gaba da rike Marcus Rashford, bayan dan wasan ya nuna kwazo a lokacin zaman aro da ya yi.
Haka kuma tattaunawa na ci gaba tsakanin Manchester United da West Ham kan dan wasa Mateus Fernandes, wanda rahotanni s**a ce yana da burin komawa Old Trafford domin ci gaba da taka leda.
Manchester United na kuma cigaba da sanya ido kan matashin dan wasan Senegal, El Hadji Malick Dioup, wanda ake hasashen kungiyar za ta iya neman daukarsa a wannan bazarar cinikayyas.